SANADIN LABARINA 4


   Free Page (4)


©®_Hafsat Rano_


** Tariq ne yake tuka motar Fauwaz na gefen sa,Baba a baya yana duba labarai a wayar sa jefi jefi suna hira da Fauwaz wanda shima rabin hankalin sa yana kan wayar sa yana duba wani pdf. Be fi sau biyu Tariq ya saka musu baki a hirar da suke ba har suka isa garin su Baban in da zasu dauko Hajiya Yaya 

   A kasan wata bishiya yayi faking kannen Baban dake zazzaune suna shan inuwa suka mike dukka suka yo wajen motar. Fauwaz ne ya bude ma Baba kofa ya matsa baya ya fito, ya shiga mika musu hannu suna gaisawa, kananan kuma suka russuna suna gaishe shi. 

   

   Cikin gidan suka dunguma suka shiga gaba daya, zuwa tsohon shashen Yayan kafin ta koma birni tun daga zuwa wani asibiti da tayi Baban yace tazo kenan, bata son birni sam amma babu yadda ta iya haka dai ta hakura bayan ya samu wasu daga cikin yan uwanta sun saka baki, duk da haka bata son zaman ta a cikin gidan sa dan ba wani shiri suke da Mama ba, ita Yaya dama bakin ta baya shiru bata gani bata tanka ba shiyasa tasu sam bata zo daya da Maman ba, tace Maman ta fiya isa da izza dan iyayenta wasu ne, shiyasa da Baba yazo mata da maganar auren Halima ta bada goyon baya dari bisa dari dan a ganin ta a lokacin ne zai auri daidai dashi.

  Hayaniyar Yayan suka fara ji tana ta fada da sababi, muryar ta a sama sosai ta dage tana fada bilhakki da gaskiya, murmushi Baba yayi, ya girgiza kansa yayi sallama a tsakar gidan, muryar sa ta sakata yin shiru ta amsa sallamar tana jefar da sandar da yake hannun ta. Fuskar Tariq a hade dan shi ba kasafai ya fiya son hayaniya da shiga cikin mutane ba duk da Baba yana tirsasa masa shiga cikin yan uwan sa dan suna da matukar yawa, yanayin sa ne a hakan kamar Safiyya, su suko yo Mama dan itama bata cika son mutane ba sai wanda tayi mugun sabo dashi. 

Shima kamar Maman ba shiri suke da Yayah ba, dan kullum yi masa korafi take bashi da sakin fuska, surutun ta shi yafi komai damun sa, dan idan ta fara magana baya jin ko hadiyar yawu tana yi. Fauwaz ne dan dakin ta da Amira, sune suka yo ta a surutu da kwashe kwashen mutane kowa nasu ne.

   Tabarma ta dauko zata shinfida musu fauwaz ya karba ya tayata, ta zauna a gefen gadon ta suka gaisa da Baban sannan su Fauwaz din suka gaishe ta ta amsa tana ficewa taje ta kawo musu ruwa ta ajiye sannan tace


"Ashe zaku zo, na dauka fa sai wani satin wallahi, ban gama abubuwan da nake anan din ba."


"Menene baki gama ba Yaya?" 


"Em.. em akwai wani biki na yar Hajara nan kasa damu, babu dadi ace ban tsaya an yi bikin dani ba."


"Ayya, sai a basu hakuri Yaya, kinga fa lokacin komawar ki wajen likita yayi har yana neman wucewa."


"A ah gaskia ba zaa basu hakuri ba, sai dai a bani gudunmawa me tsoka na bata, sai kuma ka aiko matar ka itama tazo ranar bikin da gudunmawar ta."


Tace tana yin kicin-kicin da fuska, murmushi Baba yayi yace


"An gama Yaya, sai kuma me?"


"Shikenan, sai mu tafi tun da kayi niyya, ni wallahi dan ba yadda zan ne, a kai mutum a ajiye shi waje daya haba!"


"Kiyi hakuri Yaya."


"Idan ban hakuri ba ya zanyi toh? Fatan dayafi karfin ka ai sai ka mayar dashi wasa."


    Har Kawu Rabi'u ya kawo madara da kwan zabin da ya tafi karbo wa Baba bata daina sababi ba, magaanar ta kadai kake ji a dakin sai dai Baba yayi murmushi lokaci zuwa lokaci ya amsa mata, shi kam Tariq ji yake kamar ya fice amma yasan idan yayi haka zai gamu da fishin Baba, shiyasa ya hakura ya zauna kawai yana sauraron surutun ta wanda baki daya babu magaanar da za'a kama.

   Fita Baba yayi yace zai je waje ya zauna da yan uwan sa kafin Yayan ta gama shiryawa, yana fita Tariq da ya tabbatar ya kule yaja tsaki yana dafe kansa.


"Uwarka kake wa tsaki bani ba." 


Tace tana hararar sa, kallon ta yayi idanun sa na yin kasa sosai yace


"Ni ba dake nake ba."


"Ko ma da wa kake, mutum sai kuncin tsiya ba yar fara'a haba.".


"Yaya Ya Tariq fa shine angon ki, ki dinga lallabashi." 


Fauwaz yace yana kokarin sake rura wutar fadan, buga cinyar ta, tayi tana daga murya


"Allah ya kiyashe ni da aikin dana sani, na auri mutum irin wannan ai na kade har ganye na, matar sa ta shiga uku wallahi."


"Idan kun gama ni ina waje." 


Yace yana mikewa, ta rakashi da Allah raka taki gona ya fice kawai ya bar Fauwaz yana kyalkyala dariya, da gaske dariya suke bashi musamman Tariq da ya kasa gane wasan Yayan irin wanda ake yi na tsakanin jika da kaka, da gaske yake daukar komai duk da ba kasafai ya fiya nuna fushin sa ba amma zaka ga sam baya sakewa da ire-iren wasannin.

   Shi ya taimaka mata ta karasa hada kayan ta sannan ya daukar mata jakar, suka fito ta dinga shiga waje-waje tana musu sallama tun yana bin ta har ya gaji yace yana mota. A kwance ya samu Tariq din ya kwantr da kujerar side din me zaman banza fuskarsa rufe da hular da ya saka, booth ya bude ya saka kayan Yayan sannan ya dawo ta side dinsa yayi masa magana, mikewa yayi ya fita ya bashi wajen ya koma mazaunin driver.


"Har yanzu ka kasa gane wace Yaya."


"Haka aka ce maka?"


"Ai naga kamar abun yana damunka, banda yawan maganar ta she's very nice and fun to be with, zatayi ta saka dariya ne."


"Ni kuma sai aka ce maka dariya nake so nayi ko? Bani da aikin yi sai dariya ko?"


"Ba haka nake nufi ba, yawwa gata nan ma ta fito, case closed."


Yace ya ja bakin sa yayi shiru.


"Ni zan bude kofar da kai ne kenan?"


"Afwan Hajiya Yaya, wane mutum ya bar sarauniya da bude kofa?"


Ya bude mata da sauri ya taimaka mata ta shiga, sannan ya rufe mata kofar.


"Ranki ya dade." Yace yana dariya 


"Kafi oo sau dubu, Allah dai ya baka mata ta gari me hankali da sanin ya kamata kamar kai."


"Amin."


Yace yana cigaba da dariya, Baba ne yazo ya shiga motar kusa da Yaya, sannan suka sake sallama dasu Kawu Rabi'u, Tariq yaja motar suka fita daga kauyen.


Gudu ya soma yi sosai bayan sun hau babban titi, salati Yaya ta fara yi tana salallami.


"Tariq, rage speed din nan." Baba yace yana kokarin kwantar mata da hankali


"Anya kalou yaran nan yake? Ba zaa kaishi ayi masa rukiya ba kuwa?"


Tace bayan ya rage tafiyar sosai, ta cikin rear mirror ya kalle ta, ya maida kansa gaba ya cigaba da tukin sa yana jin Baba da Fauwaz suna dariya


"Ba abin dariya bane wallahi, dole ma a nemo Malam Na Allah yayi masa rukiya gaskia."


Yana jin su yayi musu shiru tukin sa kawai yake yana fatan su isa lafiya ya tattara ya bar garin gobe dan yasan tunda ta dawo ba zata kyale shi ba sam.

   Har suka isa gida magana daya take, aikuwa yana gama parking yayi saurin fita ya dauki kayanta a booth yayi cikin gidan da sauri. Anty ce a bangaren Yayan tana karasa gyara mata sashen, ya dire jakar yana jan siririn tsaki.


"Ya akayi?" Tace masa cike da kulawa


"Kai na ke ciwo."


"Kaje akwai panadol a kan fridge ka dauka ka sha, sannu."


"Ok." Yace yayi saurin barin wajen dan baya so suzo su tadda shi, part din Antyn ya shiga, babu kowa a falon ya dauki paracetamol din ya nufi kitchen zai dau ruwa marar sanyi dan shi a rayuwar sa baya shan ruwan sanyi sai idan ana tsananin zafi. 

    Tana tsaye a jikin drawer din kitchen din tana gyaran kayan miya, kafarta ya kalla a ganta kamar kara, ya dauki ganin sa zuwa wuyanta da yayi masa kama da murkin lema, mamaki ya sake kamashi ganin tana aikin cike da kuzari, a yadda take da ramar nan be yi tunanin ko numfashi tana yin sa daidai ba, gani yake kamar ko kwakkwaran motsi tayi zata iya karyewa. Gyaran murya yayi ta juyo a tsorace, ya dauke ganin sa daga kanta ya dauki ruwan ya fice.


***Da gudun su suka fito jin sallamar Yayan, tana tsaye a tsakar gida suna gaisawa da Anty da su Abu, Amira ce ta rungumeta, tayi kamar zata yar da ita, ta tureta tana dariya


"Ke baki san kin girma bane ba? Ko dan har yanzu baki fara kirgar dangi ba?"


Kunyace duk ta kamasu, Anty tayi kamar zatayi dariya sai kawai tayi gaba tana cewa


"Yaya muje ki huta karki biye musu."


"Ai fa dan na kwaso gajiya, shima Alhaji ya rasa da wanda zai zo daukata sai da wanchan mahaukacin dan naki, ya dinga gudu dani duk yasa dan abincin da naci ya zazzage."


"Wai Tariq?"


"Kina da wani mahaukacin dan bayan shine?"


"Yanayin sa ne haka Yaya." 


"Shi kansa wanda ya gado din haka muka sha fama dashi ya buga ya barni, idan zamu kwana be ce min ufffan ba, bana tanka masa haka akayi zaman nan."


"Allah sarki, Allah yasa ya huta."


Anty tace tana ajiye mata flask din ta da aka zuba mata kunu wanda ya zama kullum sai ta shashi, saboda sabo.


"Kunu ne? Kai Allah yayi miki albarka kinji? Allah ya baki kema masu yi miki."


"Amin." Tace tana murmushi, sai kuma ta fita ta bar Amira da Umaima da Yayan 


"Welcome back granny, we missed you.!"


"Uwar granny din, na fada miki bana son sunan ko? Sai karyar turanci, toh turancin ma..."


"Ba kyau zagi fa Yaya."


"Anyi, idan ban yi ba ai ban cika bakatsiniyar ba, kuma ko gobe kika sake min turanci sai na zagi turancin, a banza a wofi wayon a zagi mutum ne."


"Bari kiga, amira sai kin taho, ni nayi gaba, Allah ya dawo da mu ai." 


Ta mike, 


"Idan kin je karki dawo, yar nema kawai."


"Almasifatu." 


Tace ta ruga da gudu, tashi Yayan tayi ta jefa mata pillow din kujera 


"Yar nema, zaki dawo har in da nake ne."


***Be shigo gidan ba sai wajen takwas na dare, lokacin Mama ta dawo, ya sameta a dakin ta, tana waya da kawarta, zama yayi akan bedside drawer ganin sa yasa ta katse wayar.


"Tariq!


Ta kira sunan sa, amsawa yayi yana kallon ta


"Ya akayi?"


Tace tana zama daga gefen gadon kusa dashi. Tun bayan da ya fara wayo halin sa ya fito sosai, babu wanda yake zama ya fadawa matsalar sa, ya sha yin ciwo a daki shi kadai babu wanda ya sani, baya taba cewa ayi masa abu sai dai ka fuskanta da kanka kayi masa amma ba wai dan ya tambaya ba, da farko halin sa ya fara tsorata ta, amma kuma kasancewar kakansa mahaifin Baban haka yake sak halin sa ya saka kawai ta hakura dan tasan biyu ce ta hadu ita kanta miskila ce. Ganin sa yanzu ya saka tasan akwai muhimmiyar magaanar da zai mata shiyasa ma ta katse wayar dan zai iya chanja shawara cikin kankanin lokaci.


"Ina jinka."


Ta sake maimaita masa tana kallon fuskar sa


"Dama na gama hada kayan tafiyar ne, sakon da kika ce zaki taho dashi daga cikin gida."


"Oh ai ban manta ba Tariq, gashi chan miko ledar chan, karfe nawa ne jirgin naka?"


"9am, amma da asubah zamu fita."


"Ok, Allah ya kaimu, ya bada sa'ar abinda aka je nema."


"Amin." Yace yana rike da ledar, be koma ya zauna ba, hakan yasa ta gane dama abinda ya kawo shi kenan.


"Nagode." 


Yace ya juya ya bar dakin, tayi murmushi kawai tana bin bayan sa da kallo.


***Da asubah bayan sun idar da sallah ya shigo cikin gidan, ya wuce shashen Anty ya kwankwasa, suna zaune bayan sun idar da sallah ita da Jidda suna karatun al'qur'ani, ta dauka Baba ne dan shine yake shigowa da asubah ya duba duk wadda ba ita ce da girki ba, tashi tayi ta bude kofar ganin Tariq yasa ta tuna da magaanar tafiyar sa 


"Ba dai har kun fito ba?" Tace tana matsa masa ya shigo ciki


Kamshin turaren sa na Versace ne ya gauraye falon, ya zauna a kujerar dake gefen kofar sannan yace


"Barka da Safiya Anty!"


"Barka dai, ka tashi lafiya?"


"Alhamdulillah, yanzu muke shirin fita, jirgin karfe tara ne."


"Ayya, Allah ya kaiku lafiya ya tsare, ya bada sa'ar abinda aka je nema."


"Amin ya Allah."


Yace yana mikewa,


"Ina kwana?"


Ta gaishe shi cikin muryar ta da take kara sashi mamakin yanayin ta, hatta muryar ta kama take da yanayin jikin ta, yar firit muryarta kamar ana busa usur. Be amsa ba sarai kuma yaji sai da Anty tace ana gaishe ka sannan yace.


"Lafiya."


A gajarce, maimakon ya tafin sa kawai ya tsaya yana nazari, wajen minti daya ya dauka yana tsaye yana juya magaanar da take masa yawo akai, kafin yace


"Anty ki kai yarinyar nan asibiti a duba ta, inaga bata da ishashiyar lafiya."


"Jidda?"


Gyada kansa yayi


"Yes, baki ganta ba? Tayi rama da yawa kar ayi iska me karfi ta tafi da ita."


Dariya sosai ya bawa Anty, ta dinga girgiza kanta cike da mamakin sa


"Toh shikenan Tariq, zan kaita."


Ajiyar zuciya ya sauke kamar wanda yayi wani aiki babba yace


"Yawwa. Sai anjima."


"Allah kaddara saduwar mu." 


Tace ya fice da sauri yana tuna lokacin da ya rage masa.

[11/25, 3:54 PM] Rano2: *_Sanadin_*


Previous Post Next Post
Sponsored Links
Sponsored Links