SANADIN LABARINA 47


 


"Come here." Ya jawota jikin sa sai kawai ta fashe da kuka, kukan da ya saka shi gaba daya yaji yayi loosing control dinsa, dama tun dazu yana ta kokarin hana zuciya da gangar jikinsa, amma sai gashi jidda na neman ballo ruwa, rarrashin ta ya ke yi amma sam taki yin shiru, dago ta yayi daga danna fuskar ta da tayi a kirjin ta, ya hade bakin su waje daya ya shiga kissing dinta da sauri da sauri.

[11/25, 3:54 PM] Rano2: _SL__**


      ©®*_*_Hafsat Rano_*_*


                  Page (47)



Malama's Citadel

08035625833

Zaria kaduna state

Original Ayu oil

Infection and Cleansing set na maza da mata

Tsumi

Tightener

Matsi me kyau

Kaza

Tsarki herbs



***Saurin hadiye kukan da take tayi ganin gaba daya Ya Tariq din ya chanja mata zuwa wani daban, yana yi mata wasu abubuwan da kwakwalwarta ya gaza dauka, gigicewa tayi ta hau kokarin tashi take ya hanata yana girgiza mata kai


"Please Jidda, dan Allah."


"Dan Allah kayi hakuri." 


Jikinta ya hau rawa kaamar mazari, ba zai iya ba, ba zai iya hana kansa ba, amma yayi alkawari zama cool, ba zai cutar da ita ba,gyara mata zama yayi a jikin sa yana shafa mata kanta, 


"Shsss, kiyi shiru kinji?, ba zai ciwo ba, I promise ba zai ciwo ba."


"Dan Allah kayi hakuri " Ta cigaba da kuka tana cigaba da son tashi, sake matse ta yayi yana cigaba da bata hakuri, har ya samu ta nutsu, tallafo fuskar ta, yayi yana kallon cikin idon ta. Motsa bakin sa yayi a hankali yace 


"Ina sonki Jidda!" 


"I love you so much, har bansan yawan son da nake miki ba, bansan yaushe ba, kawai na samu kaina in love with you, you possess all the qualities da nake son mace, i was foolish at first da na fadi abubuwan nan, and it's just my hallucination, ke nake so, only you, and you alone."


Ajiyar zuciya ta sauke tana boye fuskarta a tsakanin kirjin sa. Kansa ya daga sama yayi murmushi yana ciro ta daga chest din nasa yace


"Allow me to show you how much I love you,I promise to be a gentle man."


"Tsoro nake ji." Tace idon ta na ciccikowa


"Comman karki kuka, ba wani abu bane ba, pleaseeee."


"Kin amince?"


 Yace yana murza mata tafin hannun ta a hankali, da ka ta amsa masa duk da zuciyar ta kamar zata bud'e ta fito saboda tsabar tsoron da take ji. Murmushi ya sakar mata yana lumshe idon sa


"Thank you Jidda!" 


Yace yana gyara mata kwanciyar, kulle idon ta tayi gaba daya kukan na cigaba taso mata, tana jin kamar tace bata amince ba, kaamar tace ta fasa ya kyale ta, sai dai kash! 


    Babu irin duka da yakushin da batayi masa ba, ta dinga kiran Baffa, Aunty har Amira sai da ta kira tana neman agaji amma ko a jikin sa, be masan tana yi ba, sai jaddada mata irin son da yake mata yake da bata gane ko mai sai bakar azabar datake ji har cikin kwakwalwar. Duk da da gaske a hankali ya tafi da ita amma still ta sha bakar wahalar ,irin wadda bata taba tunani ko hasashe ba, bata san haka abun yake ba, bata kuma san yadda zata misalta ba.

    Kukan ta cigaba da yi amma k'asa-k'asa, sai jan ajiyar u yayi wajen ta tayi saurin matsawa tana rokon sa cikin muryar ta da ta dashe sosai saboda tsabar kuka.


"Dan Allah kayi hakuri wallahi ba zan iya ba."


"Ba abinda zan miki I promise, I'm sorry."


Rungume ta yayi ta cigaba da kukan yana jin ta, hannun sa na saman kanta yana shafawa a hankali, be san da wanne baki zai amfani wajen bata hakuri ba,sai kawai yayi shiru ya cigaba da shafa kan nata har ya samu tayi shiru sai ajiyar zuciya da take jerawa, rungume ta yayi kam-kam yana jin kamar ya bude zuciyar sa ya saka ta a ciki. A hankali bacci ya soma daukar ta, sai kuma zazzabin da ya dawo ya sake rufe ta, gyara mata kwanciyar yayi ya zare jikin sa a hankali ya mike ya nufi toilet yana jin kansa yayi masa nauyi sosai, ya dan jima a ciki ya fito yana goge jikin sa da towel, ya shinfida abun sallah bayan ya zura doguwar jallabiya ya dan karo fan din sannan ya tada sallah. Rara'a biyu yayi ya zauna yayi addu'a sosai sannan ya godiya Allah bisa niimar da yayi masa duk da ya saka san ransa bayan zabin Allah shine babba zabi mafi dacewa.

   Motsi yaga tana yi ya mike da sauri ya isa wajen ta, yana kallon yadda take ya mutse fuska alamun rashin jin dadi, tausayin ta yake ji gaba daya da dana sanin abinda ya aikata mata, yaso ace ba yanzu ba, yaso ace sai sun kara shakuwa sosai, amma kuma babu yadda zai. Rike ta yayi ta daina motsin ta cigaba da baccin a wahalce, jikin ta zafi sosai kamar wuta, so yake ya taimaka mata ya rage mata zafin jikin amma baya so ta tashi a gigice dan duk ta riga ta tsorata dashi. Magungunan ta yaje ya dauko yazo ya ajiye a bedside ya hau gadon a hankali yadda ba zata tashi ba,  ya kwanta a bayan ta ba tare da ya hada jikin sa da nata ba, ya leko fuskar ta ya gyara mata gashin ta da ya hargitse ya bazo har saman fuskarta.

   Wajen asubah ta farka ta ware idon ta akan shi sai abinda ya faru ya dawo mata, da sauri ta sake matsawa daga kusa dashi, ta sakko a hankali daga gadon tana ya mutse fuska ta shiga toilet, karar bud'e kofar toilet din ce ta tashe shi, ya kalli bangaren datake kwance ganin bata nan yasa ya tashi da sauri ya bi bayanta ya bud'e toilet din da turo shi kawai tayi bata rufe ba. Tana tsaye tana hawaye ya shigo, ya riko ta yana kiran sunn ta


"Jidda?"


"Menene? Akwai abinda yake miki ciwo ne?"


Daga kanta tayi tana jan kukan, 


"I'm sorry dan Allah kiyi hakuri."


"Ni ka fita." Tace tana cigaba da kukan, 


"Taimaka miki zan, zaki ji sauki."


"Um um ni bana so."


"Kiyi hakuri dan Allah, ki bari na taimaka miki kinji?"


Noke kafardar ta tayi, 


"Shikenan, shikenan zan fita, I'm sorry."


Sai ya juya ya fita ya ja mata kofar, ya cire bedsheet din ya saka a gefe ya dauko wani a closet ya saka sannan ya dawo ya tsaya a jikin kofar yana jiran ta fito, ta dade sosai har ya fara tunanin komawa ciki amma sai gata ta fito tana jan kafar ta, yayi saurin tarar ta, ya kai ta ta zauna a gefen gadon ya dauko towel ya hau goge mata kanta. 


"Sanyi." 


Tace tana kankame jikin ta, saurin kashe komai yayi ya bud'e kayan sa,ya dauko mata jallabiyar sa, ya saka mata sannan ya taimaka mata ta kwanta, kumburarrun idon ta ya kalla ya girgiza kai lokacin aka soma kiran sallar asubah, alwala yaje yayi yazo yace ta tashi suyi sallah, ta mike tana kin kallon sa ya bata Hijab ta saka har lokacin sanyi take ji sosai sukayi sallar sannan ta koma ta kwanta ya lullube ta ya fito zuwa kitchen ya hado mata tea me kauri ya dawo dakin ya tashe ta zaune tasha sannan ya bata magungunan ta,tasha suma sannan ta koma ta sake kwanciya, bata dade ba baccin ya sake dauke ta. 

   A gaban gadon saitin fuskar ta ya durkusar da guiwowin sa yana kallon kyakkyawar fuskar ta da tayi ja saboda tsabar kuka, saman dogon hancin ta ya kai hannu wajn wani ja ya taba kad'an yana girgiza kansa, a yadda take fitar da numfashin ya tabbata taji jiki sosai, dama kuma ga ciwon targaden da ya dinga kokarin hana kanshi akan hakan amma be san me ya hau kansa ba, ya kasa hakura bayan yasan tana bukatar tayi healing yazo ya kara mata wani ciwon akan wanda take fama, be kyauta ba sam, kuma zata iya yi masa wani irin kallo. Hannun sa ya kai ya shafi gefen fuskar ta.


"I love you Little Jiddah."


 Sai yayi kissing dinta a saman goshin ta, sannan ya mike ya fita daga dakin ganin rana ta fito sosai.




***Wayarsa dake yashe akan kujera tun sanda Yasmin ta kirashi ya ajiye be saka bi ta kanta ba ya dauka ya ga missed calls da yawa, da sauri ya cire lock din ya shiga call log ya tarar da 15missed calls daga Yasmin sai 5 daga Mama sai Fauwaz guda biyu. Duk da dama yasan Mama zata kirashi amma be yi tunanin har missed calls haka ba, kiran ya bi yana kishingid'a a saman kujerar yasa hannun sa yana shafa saman kansa dake masa ciwo sama-sama.

   Bata dauka ba har ta katse ya sake kira nan ma no answer sai kawai ya ajiye wayar yana tunanin yadda zasu kwashe da maman yana kuma fatan ta fahimce shi ko yaya ne. Wani tunani ne yazo masa sai ya sake daukar wayar ya kira Fauwaz bugu daya ya daga.


"Ya Tariq ina ka shiga?"


"Fauwaz, bacci nayi na bar wayar a falo naga miss calls din Mama da yawa, hope lafiya?"


"Ba kalou ba wallahi, akwai babbar matsala."


"Toh! Me ya faru?"


"It's a complicated case wallahi, ni dai da zaka zo gidan yanzu kawai."


"Jidda bata jin dadi ba zan iya barin ta ba, she needs me."


"Ayya, Allah ya bata lafiya, kaga Maman ma gasu nn sun fito ita da Aunty Nafi da Salma, bari naji zan kiraka."


"Ok, kace wa Maman na kirata bata daga ba."


"Okh ." Yayi hanging yana nufar wajen su, 


"Mama,fita zakuyi?"


Wani kallo tayi masa ya sunkuyar da kansa k'asa dan yasan halin da Maman take ciki ba karami bane ba


"Tariq be kiraka ba?"


"Ya kira, ya kira ki ma baki daga ba."


"Good, idan ma yayi hakan ne dan kar mu hadu ni yanzu zanje har gidan nasa na same shi."


"Gida kuma Mama? Why not ki bari yazo, za'a iya solving issue din nan ba sai kinje ba."


Kallon shashen da Aunty Nafi da Salma ke tsaye tayi ranta ya kara baci idan ta tuno da abinda Salmar tace wanda tasan sharri ne kawai tayi wa Tariq din kuma da tainakon Nafin da tasan haka zasu yi mata da tun farko bata yarda da shawarar Nafin ba.

   

"Ina Sam?" Tace tana share maganar Fauwaz din, da sauri ya karaso ya duka ya gaishe ta, 


"Muje." 


"Mama bari na kaiku."


"Zaka iya biyo bayan mu, ku shiga muje."



 Tace wa aunty Nafi ta shiga ita,zagaya wa sukayi Salma ta shige chan baya, security daya ya zauna a gaba sai Mama da Aunty N a tsakiya. Da sauri Fauwaz ya nufi wajen motar sa ya shiga yana kiran Ya Tariq din a waya amma sam taki shiga, key yayi ma motar ya bi bayan su yana cigaba da gwadawa.

  

  Yana kwance a falo lokaci zuwa lokaci yana lekawa ya dubo Jiddan amma sai yaga tana bacci, sai ya dawo. Har bacci ya soma daukar sa yaji ana knocking a chan kofar main entrance din, Godiya ce ta fito daga kitchen taje ta bud'e sai ya mike ya fito daidai lokacin da Mama, Aunty Nafi, Salma sai Fauwaz dake bayan su suka shigo, da kallo ya bisu irin kallon mamakin nan, kafin ya karaso yana nazarin fuskar Maman da take a hade tamkar an mata mutuwa.


"Mama? Welcome."


"Ina ka ajiye wayar ka nake da kiran ka?"


"A falo na barta."


"Good, zauna." Tace tana nuna masa wajen zama ya zauna a darare duk jikinsa yayi sanyi dan be san dalilin zuwan nasu ba


"Salma, maimaita abinda kika fada mana ni da mamanki."


"Na'am?" Tace tana kallon TARIQ din da itama shi yake kallo


"Kiyi magana mana ba kallon sa zaki tsaya yi ba." Aunty Nafi tace tana tamke fuska


"Dama, dama ya Tariq ne."


Saukar da kai Mama tayi wani irin abu na taso mata tun kafin Salman ta yi maganar da ta gigita ta, ta kuma hanata bacci a daren jiya ko runtsawa bata yi ba.


"Muna jinki."


"Dama shine ya ke taba ni yana min wani abu shine jiya da ya dawo ya fara min wata irin magana ni kuma nace bana so sai ga jiddah nan ta fito shine ya kore mu yace mu bar masa gida."


   Wajen sakwanni biyar maganganun nata suka dauka kafin su kai sakon zuwa kwakwalwar Tariq wanda ya kura mata ido kawai ya kasa furta ko kalma daya.


"Kaji abinda tace?"


 Mama tace cike da kunya da takaicin hali irin na Nafi 


"Ya Tariq kana ji kuwa?"


 Fauwaz yace ganin kamar be san me ake cewa ba.

Previous Post Next Post
Sponsored Links
Sponsored Links