DAUDAR GORA 10

 


𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲      



  ✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨

           (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)




            𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻



*_10_*



........Kamar wasa Iffah na shigowa gida ta zube kwance tana rawar sanyi, ga jikinta ya ɗauka matsanancin zafi. Ummu bata kawo komai a ranta ba game da ciwon Iffah sai tunanin ranar da ake ƙwallawa ce ta washeta. Da ƙyar ta tilastata tai wanka, taci abinci kaɗan ta ajiye. Maganin zazzaɓi Ummu ta bata tasha, daga haka ta koma ta kwanta ranar ko Islamiyya bataje ba.

      Da dare firgita data dingayi saboda munanan mafarkai ya sa kusan kowa bai rintsa ba a gidan sai gab da asuba. Da barci yaɗan figeta saita tashi a firgice har sai sun rufeta da addu'oi take samun nutsuwa ta sake komawa barci. Al'amarin ya tsayama kowa a rai, sai dai ganin ta tashi ragal da asuba tai salla sai sukaita mamaki. Dan bazaka taɓa tsammanin itace a daren jiya ba.

        Da safe koda tace zataje makaranta hanata Babiy yayi, acewarsa ma asibiti zasuje da Hanash. Kasancewar Iffah da rashin son asibiti sai ta turje akan itafa ta warke, dama jiyan rana ce (ta fake da abinda Ummu tace). Ganin harda ƴan kwallanta Babiy yace to inhar zazzaɓi ya sake dawowa a yinin yau dole suje asibitin nan. Da sauri tace ta yarda. Bayan wucewar Babiy tai ta ɗan ƙarfafa kanta harda taya Ummu aiki, duk da yanda takejin yanayinta babu daɗi haka tai ƙudirin shirin Islamiyya idan lokaci yayi, tana ɗaki kwance bayan idar da sallar azhar sai ga kiran   malaminta Fawzan, wayar kawai ta tsurama ido tamkar bazata ɗauka ba harta katse, wani kiran ya sake shigowa shima harya katse bata ɗaga ba. Duk da zumuɗin son ganin kiran nashi da take ciki a kusan kwanaki uku sai taji hanunta ya mata nauyin ɗagawa a yanzu daya kira... Shigowar saƙo ya katse mata tunani, ta kai hannu kan wayar ta ɗauka kamar mai tsoro...

      _“Fareedah ga dama ta biyu ta sake samuwa, Idan kinga saƙona kiyi ƙoƙarin fitowa kafin Four”._

     A zabure ta miƙe jikinta na tsuma ta hau shirin Islamiyya, tare da tattare dukkan takardun bayanan da take ta faman adanawa harma da waɗanda ta ƙara haɗawa a kwanaki ukun nan. 

           “Ummu zan wuce Islamiyya”. Ta faɗa lokacin da take ƙoƙarin saka takalmi a ƙafarta Ummu na tsakar gida tana alwalar sallar la'asar. 

     “Ke da baki da lafiya auta”.

“Ummu naji sauƙi wlhy, kinga saukarmu ya kusa babu buƙatar na fara wasa ai. Malam nata mana gargaɗin hak......”

     Sauran maganar ya maƙale a harshenta sakamakon tashin sautin busa mai nuni da isowar jama'ar masarautar Daular Ruman. Tamkar an daki kan Iffah da guduma haka taji wani dummm! A cikin kunnenta har suka ƙarasa shigowa cikin gidansu jinta bai dawo ba. (Shin tsoro ne? Ko firgici?) bata san wanene ya risketa ba...... Taɓata da Ummu tayine ya sata jan kakkauran numfashi tare da kallonta. Jikin Ummu ne ke rawa, idanunta kam tuni sun tara ƙwalla. Iffah ta shiga girgiza mata kai alamar kar tai kuka, ta sake damƙe hanunta cikin nata tare da maida kallonta garesu rai ɓace, dan ta ɗauka alwashin a wannan karon komi sukazo da shi sun tara sun samu, sai dai a kasheta...

      “Mi kukazo yimana a gida kuma? Ko kun dawo muma ku idasa kashemu tamkar yanda kuka halaka min ƴan uwana da tsafink......”

   Da sauri Ummu ta danne mata baki da tafin hannunta tun kan ta ƙarasa faɗa. Kai take girgizamata cikin rawar jiki. Da ace ba Ummu bace babu abinda zai hanata ta ture hanunta ta ƙarasa abinda ta fara faɗa ko zata samu salama a ranta. Sai dai kuma bazata iya ba, dan haka ta shiga yima Ummu alamar roƙo da magiyar ta barta amma taƙi yin hakan...

         Basamuden nan ne na kullum mai riƙe da bulala ya daka mata tsawa. Da sauri Ummu ta sakemata baki, sai dai ta jawota jikinta ta ƙanƙame. Iffah jitai zuciyata ta ƙara hautsunowa, a matuƙar zabure ta sake buɗe baki zatayi magana ya dakatar da ita...

    “Ke ƴar talakawa lura da inda kike. Bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane. Idan taƙamarki tsageranci tamkar ƙiftawar ido za'a sauke miki shi, a kuma shafe babinku daga ke har iyayen naki a doron ƙasa”.

      Hasala iya hasala Iffah tayi, Kukan da Ummu ta fashe da shi ya hanata cewa komai ta juya gareta jikinta na rawar shiga tsananin ɓacin rai, kanta take juyamata alamar karntace komai.....

    “Umm....”

“A'a Iffah! Ina umartarki karki ce komai”.

         “Kibarta tace ɗinma yanzu harshenta ya zama datsatstse a gabanki.”

     Kafin Ummu dake girgiza kai tace komai Babiy ya shigo tamkar an jehoshi, da alama dai wanine ya sanar masa da zuwan jama'ar masarauta gidan nasa. Ko sau ɗaya basu bashi damar cewa komaiba suka isar masa da saƙon kira daga daular ruman.

     “Innalillahi.....” Iffah ta shiga ambata ita da Ummu, dan sunaji a ransu tarihine dai yake ƙoƙarin maimaita kansa, hawaye masu tsananin ƙuna da ɗaci na gangarowa bisa ƙyaƙyƙyawar fuskata Babiy da shima dai yasan labarin gizo bazai wuce ƙoƙi ba. A gaban idonsu aka wuce da Babiy Daular Ruman a karo na uku, tare da barin wasu dakaru a ƙofar gida ta hanyar hana duk wani mai yunƙurin fita daga gidan. Haɗe kai kawai Iffah da Ummu sukai suna kuka, dan shi kaɗai suke da damar yi ɗin..


       ★Bayan cikar awanni biyu da tafiyar Babiy sai gashi ya dawo, dawowa irin wadda ya saba a duk lokacin da makamancin kira irin wannan ya samesa daga daular Ruman. Yanda ya kafe Iffah da idanunsa dake zubda hawaye ya saka Ummu zubewa ƙasa cikin kuka. “Abu Hanash itama zamu rasata ko? Itama ka ɗaura mata aure da Tajwar.....?”

       Hawayene masu ɗumi da ƙuna suka ziraro a idanun Babiy, ya girgizama Ummu kansa a hankali alamar a'a, tare da girgiza kan nasa kuma alamar tayi shiru. Hawayen nata ta share kamar yanda ya buƙata, sai dai jikinta bai bar tsuma ba. Kamar yanda Iffah data kafesa da idanu bata iya ko ƙyaftawa ba. Ummu ta sake gyara zamanta da fuskantar Babiy da ƙyau....

     “Idan ba abinda muke tunani bane to minene ya faru?”.

   “Ki kwantar da hankalinki babu komai f.....”

  “Bazan taɓa yarda babu komai ba. Sai dai idan kana so ka rufeni ne. Hakan kuma shine mafi ƙololuwar kuskuren da banajin zan iya yin afuwa gareka a kanshi. Dan inaji a jikina zuwanka masarauta nada nasaba da rayuwar yarinyata data rage min, idan har zuciyarka ta iya ɓoyewa ƙwayoyin idanunka basu lulluɓe komai ba, garama ka sanar min”.

      Babiy ya fahimci idon Ummu ya rufe ta manta Iffah na wajen, dan haka ya cigaba da ƙoƙarin ganin ya kufcema faɗar abinda yazo da shi har sai sun keɓe amma ta dage akan itafa ya faɗa mata a yanzu. So yake ya buɗe ido amma bashi da sauran ƙarfin zuciya a yanzu, dan haka a sanyaye ya rumtse idanunsa da launinsu yay matuƙar komawa ja. “Ba'a ɗaura mata aure da shi ba. Sai dai....” ya kasa ƙarasawa.

    “......Sai dai me? Dan ALLAH ka faɗa min”. Ummu ta faɗa tana mai sake fashe masa da kuka mai matuƙar sake ɗaga masa hankali. Miƙewa yay yunƙurin yi tai saurin riƙe masa ƙafa. Babiy ji yake shima kamar ya fashe da kuka ya huta kawai. Ya dawo ya durƙusa gaban Ummu tare da riƙo mata hannu, “Akan abinda suka faɗa munada mafita tunda yasha ban-ban dana baya Jumaima. Dan haka na gama yanke shawarar zamu bar garin nan dama ƙasar gaba ɗaya a daren yau insha ALLAH. Dan sun buƙaci izinin neman auren Iffah ne a gareni, sun kuma bani damar zuwa nai shawara daga nan har zuwa ƙarshen makon nan”. 

      Kafin Ummu ta samu damar cewa wani abu sulalewa da faɗuwar Iffah a lokaci guda ta riski kunnuwansu. A tare suka zabura kanta jikunansu na matuƙar rawa da tsuma. Ummu ta fashe da kuka dai-dai tana ɗago Iffah dake wanwar a ƙasa taga ta koma yaraf alamar babu rai a tare da ita.....


     .....Sosai kukan Iffah ya sake ɗaga hankalin Babiy. Dan tunda aka zuba mata ruwa ta farfaɗo ta haɗe kai da gwiwa. Suma idanu kawai suka zuba mata suna hawayen zuci, rikicin yana a kantane kawai, amma sune suka fita jin raɗaɗin a zuciya saboda ita akwai ƙuruciya tare da ita. A ganinsu bai zama lallai ma tana hange irin wanda su suke matane ba.

      Kusan mintuna talatin suna a haka, kafin Babiy yay ƙarfin halin miƙewa suma yay musu umarnin su tashi su koma ciki. Sai da taimakon Ummu Iffah ta iya miƙewa, har sun kusa shiga ɗakin ta tsaya, ɗagowa tai ta dubi Ummu ta juya ta dubi Baby hawaye na sauka da gudu bisa ƙyaƙyƙyawar fuskarta.

      “Bazamu gudu ba Babiy, zan aure shi....”

   Kaɗan ya rage Babiy yaci uban tuntuɓe saboda firgitaccen furicin Iffah mai kamanceceniya da gawurtaciyar sautin saukar aradu cikin tsakkiyar duhuwar dare. Ummu ma dai da taima Iffah sakin bazata ƙirji ta dafe dukanin idanunta na firfitowa.....

        Iffah ta share hawayenta da sakin murmushi a karo na farko. “Ummu! Babiy! ku kwantar da hankalinku, kar kuma ku ɗauka ba'a cikin hayyacina nake ba. Nasan burinku shine ku kuɓutar dani daga mutuwa, sai dai kuma a duk inda zanje ku sani tana tare da nine. Wannan azzalumin ba guje masa ya kamata ayi ba, tunkararsa ya kamata ayi. Kamar yanda kaka ya faɗa, a wasu lokutan gujema ƙaddara ba mafita bace sake kirawowa kai halaka ne. Amma tunkararta gaba da gaba ƙarfafa imani ne sannan jarumtace. Shin idan mun gudu kunada tabbacin zamu iya tsere musu bayan ƙasar a hanunsu take? Sannan idan mun tafi ina zamuje bayan babu inda muka sani sama da ƙasar Ruman. Fir'auna ma da yay nasa zamanin mulkin da ko kama kafarsa wannan shaiɗanin baiyiba UBANGIJI maida ANNABI MUSA (A.S) yay cikin gidansa ya rayu bisa ƙudirarsa da tabbatar masa shine mai iko akan kowa da komai. Azzalumin nan ba gudun masa ya kamata ayi ba, daƙilesa ya kamata ayi, domin idan ni kun kuɓutar dani, su sauran iyayen da zasu iya fuskantar makamancin halin da kuke ciki fa bayanku?. Babiy zanyi biyayya kamar yanda ƴan uwana sukayi, kuma ku sani da iznin ALLAH nice zan kashes........”

   Cikin rawar jiki Ummu ta zaburo tare da toshe bakin Iffah. Sai faman waigen bayansu take domin sanin dakarun Daular Ruman na ƙofa gidan har su biyar. Babiy ma gaba ɗaya kalaman Iffah sun sake rikitashi. Sai dai kafin wani cikinsu ya samu damar cewa wani abu ta shige cikin ɗakin. Idanu suka tsirama juna shi da Ummu harna tsahon mintina biyu, kafin Babiy yay ƙarfin halin janyewa yana mai jan nannauyan numfashi da barin wajen ya shige ɗakinsa. Da ƙyar itama Ummu ta sauke numfashin, har zatabi bayan Iffah sai kuma ta fasa ta nufi ɗakin Babiy ɗin itama.


        Shigowarta dai-dai dayin sallamarsa waya manne a kunensa. Zaune takai a bakin gadon dake ɗakin dan inba haka ba zata iya zubewa ƙasa saboda yamutsawa da jininta ke mata. Jin sunan Baba da Babiy ya ambatane ya sata maida hankali garesa itama. Komai sai da Babiy ya zayyanema Kaka kafin yay shiru alanar saurarensa.

     Daga can Baba yaja nannauyan numfashi bayan gama sauraren surukin nasa mijin ƴarsa tilo data rage masa a raye. Sai kuma yay murmushin ƙarfin hali mai sautin daya isa har cikin kunnen Babiy. “Ni ma ina goyon bayan maganar Fareedatu. Da ace wani rai nada ikon hana tabbatuwar wasu daƙiƙu na gaban rayuwarsa masu tafe da ƙaddara da mutane da yawa sunyi rigakafi kafin cikar adadin waɗan nan daƙiƙu Muhammadu Zayyanu. Amma inaso ku tuna muɗin talakawansu ne, masu rayuwa a ƙarƙashin mulkinsu, bamu da wani ƙarfin iko akan hukuncinsu garemu ko kan ƴaƴanmu. Dan haka ku bita da addu'a kawai itama.”

       Tamkar yana gabansa ya jinjina masa kansa, tare da ƙoƙarin danne hawayen da yake na zuciya da ƙunarsu gara ace a zahiri suke zuba bisa ƙyaƙyƙyawar fuskarsa. “Shikenan Baba, amma furucin Iffah ya girgizani, ina tsoron kar zuciya ta ingizata tai yunƙurin aikatawa. Kisa fa! Koda bata aikata ba fitar wannan furucin zuwa kunen wani bayan mu ba ƙaramar magana bace”

     “Kar komai ya dameka Muhammad Zayyan. Ta faɗane kawai saboda raɗaɗi da takeji da kuma ƙuruciya, kai dai ka sanar dasu ka amsa daga nan zuwa kwanaki uku. Zan zo a amsa kuɗin auren da ni dama wasu a cikin zuri'an ka insha ALLAHU.........✍


Previous Post Next Post
Sponsored Links
Sponsored Links