Dan Shugaba Buhari: Yusuf zai angon ce da amaryarsa yar gidan sarauta

Yusuf Buhari, dan shugaban kasa Muhammadu Buhari, na shirin auren yar gidan sarkin Bichi a jihar Kano, Nasiru ado Bayero.



zahra Bayero a yanzu haka daliba ce a kasar Burtaniya, tana karantu a fannin tsarin gine-gine.

Yusuf ya kammala karatun Digirin sa a shekarar 2016 a jami’ar Surrey, Guildford, United Kingdom.

Wasu majiyoyi masu tushe sun fada wa jaridar DAILY NIGERIAN cewa za a yi bikin auren “a cikin watanni biyu zuwa uku masu zuwa”.

“Shirye-shirye suna kan hanya. Kamar yadda al’adar ta tanada, iyayen ango sun hadu da iyayen amarya don bayyana sha’awar Yusuf na auren Zahra, ”majiyar ta ce, tana neman a sakaya sunan ta.

Majiyar ta kara da cewa da tuni an gudanar da taron amma saboda rashin mahaifiyar ango, Aisha Buhari, wacce ba da jimawa ba ta dawo daga tafiya neman lafiya ta watanni shida a Dubai.

“Yanzu da mahaifiyarsa ta dawo ‘yan makonni kadan Suka rage zuwa watan Ramadan, ya bayyana a fili cewa za a yi bikin bayan hutun Sallah,” in ji majiyar.

A ranar 27 ga Disamba, 2017, Yusuf ya yi mummunan hatsarin babur a kusa da yankin Gwarinpa na Babban Birnin Tarayya, Abuja.

Ya samu kwanciyar dubiyar likitoci na kimanin wata daya a asibitin Abuja kafin a kai shi kasar waje domin yi masa magani. Ya dawo Najeriya daga jinya a ranar 1 ga Maris, 2018.

Ga Hotunan Budurwar da zai aura danna hoton dake kasa domin kallonsu kai tsaye





Previous Post Next Post
Sponsored Links
Sponsored Links